A Najeriya, yayin da ƙananan ma`aikata da
sauran masu ƙaramin ƙarfi ke neman hanyar
mallakar muhalli ido-rufe, wasu gidajen da
gwamnati jihar Kano ta gina sun kama hanyar
yin kwantai.
Har yanzu dai mutane ba su shiga rukunin
gidajen Kwankwasiyya City da Amana City da
kuma Bandirawo City ba, wadanda gwamnatin
Engineer Rabiu Musa Kwankwaso ta gina.
Wani mai ƙaramin ƙarfi a jihar Haruna Ado
Umar ya ce ya kan ji matukar taikaci idan ya
ga gidajen babu kowa a ciki.
'Babu yadda za'a yi mai ƙaramin ƙarfi ya
mallaki gida na miliyan 27', in ji shi.
Gwamnatin Ganduje dai ta ce ta gagara sayar
da gidajen ne saboda masu ƙaramin ƙarfi na
kukan cewa sun yi matukar tsada.
Ta kara da cewa tuni da dukufa wajen gina
wasu sabbin gidaje masu daki uku-uku da ake
sayar da su akan Naira miliyan biyu da dubu
dari takwas da hamsin wadanda masu
ƙaramin ƙarfin zasu iya saye.
Sai dai wasu masana sun ce kamata ya yi a
bada hayan gidajen da ba'a sayar ba
kasancewar sun yi tsada ga masu son saye.
Turawa zuwa Ka Ajiye comment A Qasa....
Nigeria: Me ya sa aka kasa sayar da gidajen Kwankwasiyya?Created at 2017-05-11 11:09:06
Tags: Nigeria: Me ya sa aka kasa sayar da gidajen Kwankw 0
Rate up Star Share: